Aya :
1
وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.
Aya :
2
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?
Aya :
3
ٱلنَّجۡمُ ٱلثَّاقِبُ
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.*
Aya :
4
إِن كُلُّ نَفۡسٖ لَّمَّا عَلَيۡهَا حَافِظٞ
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.
Aya :
5
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?
Aya :
6
خُلِقَ مِن مَّآءٖ دَافِقٖ
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.
Aya :
7
يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.
Aya :
8
إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.
Aya :
9
يَوۡمَ تُبۡلَى ٱلسَّرَآئِرُ
Rãnar da ake jarrabawar asirai.
Aya :
10
فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٖ وَلَا نَاصِرٖ
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).
Aya :
11
وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجۡعِ
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.
Aya :
12
وَٱلۡأَرۡضِ ذَاتِ ٱلصَّدۡعِ
Da ƙasa ma'abociyar tsãgẽwa,*
Aya :
13
إِنَّهُۥ لَقَوۡلٞ فَصۡلٞ
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki*
Aya :
14
وَمَا هُوَ بِٱلۡهَزۡلِ
Kuma shĩ bã bananci* bane
Aya :
15
إِنَّهُمۡ يَكِيدُونَ كَيۡدٗا
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.
Aya :
16
وَأَكِيدُ كَيۡدٗا
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.
Aya :
17
فَمَهِّلِ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَمۡهِلۡهُمۡ رُوَيۡدَۢا
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.